Luke 2:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُواْ، أَوَنَّنْ لُواْكَثِ أَݣَويْ وَنِ مُتُمِنْ دَيَكٜىٰ ذَمَ أَ عُرُوشَلِيمَ دَ عَكٜىٰثٜىٰ دَشِ سِمٜىٰيُوانْ؞ شِے مُتُمْ مَيْ أَدَلْثِنٜىٰ، مَيْ بَوْتَرْ اللَّهْ ، كُمَ يَنَ جِضَانْ رَانَرْ دَ ذَاعَ ثٜىٰثِ إِسْرَٰٓءِيلَ؞ رُوحُ مَيْ ڟَرْكِے كُوَ يَنَ تَرٜىٰدَشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
To, akwai wani mutum a Urushalima, mai suna Saminu, adali, mai bautar Allah, yana kuma ɗokin ganin ta'aziyyar Isra'ila. Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.