Luke 2:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يُوسُڢَ مَا يَبَرْ غَرِنْ نَظَرٜىٰتْ عَثِكِنْ غَلِيلِ يَجٜىٰ غَرِنْ بَيْتَلَحْمِ عَيَنْكِنْ يَهُودِيَ، وَتُواْ غَرِنْ دَ عَكَ حَيْڢِ سَرْكِے دَاوُدَ كٜىٰنَنْ؞ يُوسُڢَ يَجٜىٰ ثَنْ دُواْمِنْ شِ دَغَ دَنْغِنْ دَاوُدَ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yusufu shi ma ya tashi daga birnin Nazarat, a ƙasar Galili, ya tafi ƙasar Yahudiya, ya je birnin Dawuda, da ake kira Baitalami (domin shi daga gidan Dawuda ne, na cikin zuriyarsa),