Luke 23:46 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِيسَىٰ يَطَغَ مُرْيَ دَ ڧَرْڢِے يَثٜىٰ «عُبَا! عَثِكِنْ حَنُّوَنْكَ نَكٜىٰ بَادَ رُوحُنَ؞» دَ يَڢَطِ حَكَ، سَيْ يَجَا نُمْڢَشِنْسَ نَڧَرْشٜىٰ يَمُتُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Ya Uba, na sa ruhuna a ikonka.” Da ya faɗi haka kuwa, sai ya cika.