Luke 3:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
رُوحُ مَيْ ڟَرْكِے يَسَوْكُواْ عَكَنْسَ عَكَمَنِّنْ كُرْثِيَ؞ سَيْ عَكَجِ وَتَ مُرْيَ دَغَ سَمَ تَثٜىٰ «كَيْ نٜىٰ طَانَ، وَنْدَ نَكٜىٰ ڧَوْنَ؞ إِنَ جِنْ دَاطِنْكَ ڨُورَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa da wata kama, kamar kurciya. Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Kai ne Ɗana ƙaunataccena, ina farin ciki da kai ƙwarai,”