Luke 4:36 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دُكَنْ مُتَنٜىٰ سُكَ كَامَ بَاكِ كَوَيْ، سُنَ ثٜىٰ وَجُونَنْسُ «وَنٜىٰ إِرِنْ أَبُنٜىٰ حَكَ؟ دَ ڧَرْڢِے دَ إِيكُواْ وَنَّنْ مُتُمْ يَعُمَرْثِ ڧَظَامَنْ رُوحُواْحِ حَرْ سُنْ ڢِتَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai mamaki ya kama su duka, suna ce wa juna, “Wannan wace irin magana ce? Ga shi, da tabbatarwa, da gabagaɗi kuma yake umartar baƙaƙen aljannu, suna kuwa fita.”