Luke 6:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِيسَىٰ يَسَوْكُواْ تَرٜىٰدَ مَنْذَنِّےنْسَ، يَڟَيَ أَوَنِ وُرِے مَيْ ڢِيلِ سُواْسَيْ، تَرٜىٰدَ مُتَنٜىٰ دَيَوَ وَطَنْدَ سُكٜىٰ أَلْمَجِرَنْسَ؞ أَ نَنْ كُمَ غَا مُتَنٜىٰ دَيَوَ دَ سُكَذُواْ دَغَ كُواْعِنَ عَيَنْكِنْ يَهُودِيَ دَ عُرُوشَلِيمَ دَ كُمَ يَنْكِنْ غَرُضُوً تَيَ دَ سِدُوانْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ عَبَاكِنْ بَبَّرْ تٜىٰكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya gangaro tare da su, ya tsaya a wani sarari. Ga kuwa babban taro masu binsa, da kuma taro masu yawan gaske daga duk ƙasar Yahudiya da Urushalima, da kuma yankin ƙasar Taya da Sidon da yake bakin bahar, waɗanda suka zo su saurare shi, a kuma warkar da cuce-cucensu.