Luke 6:49 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا دُكْ وَنْدَ يَجِ مَغَنَاتَ بَيْكُمَيِ أَبِنْدَ نَثٜىٰ يَيِبَ دَيْدَيْ يَكٜىٰ دَ مُتُمِنْدَ يَغِنَ غِدَنْسَ بَاتَرٜىٰدَ يَيِ وَغِدَنَّنْ تُوشٜىٰ مَيْݣَوْبَ؞ دَ عَكَيِ أَمْبَلِيَرْ ضُوَ، سَيْ تَبُغِ غِدَنْ، سَيْ يَڢَاطِ غَبَاطَيَ؞ ڢَاطُوَرْ غِدَنَّنْ كُوَ تَيِ مُونِ سُواْسَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma wanda ya ji maganata, bai kuwa aikata ba, kamar mutum yake wanda ya gina gida a kan turɓaya, ba harsashi. Ruwan kogi ya buge shi, nan da nan ya rushe. Wannan gida ya yi mummunar ragargajewa!”