Luke 7:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ya amsa wa almajiran Yohanna ya ce, “Ku koma ku faɗa wa Yohanna abin da kuka ji, da abin da kuka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin bishara.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِيسَىٰ يَأَمْسَ مُسُ يَثٜىٰ «كُكُواْمَ كُغَيَ وَ يَحْيَى أَبِنْدَ كُكَجِ، كُكَ كُمَ غَنِ، وَتُواْ مَكَڢِ سُنَ سَامُنْ غَنِ، غُرَغُ سُنَ تَڢِيَ، مَاسُ ثُوتَرْ ڢَتَرْ جِكِے سُنَ سَامُنْ وَرْكٜىٰوَ، كُرَمٜىٰ سُنَجِنْ مَغَنَ، أَنَتَادَ وَطَنْدَ سُكَ مُتُ، أَنَ كُمَيِ وَتَلَكَاوَا وَعَظِنْ لَابَرِ مَيْ دَاطِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka ji da abin da kuka gani. Makafi na samun gani, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara.