Luke 8:47 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَمَاتَرْ تَغَ دَيْ أَنْ‌غَانٜىٰتَ، سَيْ تَڢِتَ، جِكِنْتَ يَنَ ضَوَ، تَڢَاطِ أَغَبَنْ عِيسَىٰ ؞ تَا كُمَ بَيَّنَ مَسَ أَغَبَنْ كُواْوَ دَلِيلِنْ دَيَسَا تَتَٻَشِ دَ يَدَّ تَوَرْكٜىٰ نَنْ تَكٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da matar ta ga ba dama ta ɓuya, sai ta matso tana rawar jiki, ta fāɗi a gabansa, ta bayyana a gaban duk jama'a dalilin da ya sa ta taɓa shi, da kuma yadda ta warke nan take.