Luke 9:33 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da mutanen na barin Yesu, sai Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. Bari mu kafa bukkoki guda uku, wato, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.” (Bai ma san abin da yake faɗi ba.)
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ مُتَنٜىٰنَّنْ ذَاسُبَرْ عِيسَىٰ كٜىٰنَنْ، سَيْ بِتْرُسْ يَثٜىٰ مَسَ «مَيْغِرْمَ، يَيِݣَوْ دَمُكٜىٰ أَنَنْ! بَرِ مُيِ بُكُّواْكِ عُكُ، طَيَ دُواْمِنْكَ، طَيَ دُواْمِنْ أَنَّبِے مُوسَٰى، طَيَ كُمَ دُواْمِنْ أَنَّبِے إِلْيَاسُ؞» بَيْ مَا سَنْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ڢَطَابَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutanen nan na rabuwa da shi ke nan, sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Maigida, ya kyautu da muke nan wurin. Mu kafa bukkoki uku, ɗaya taka, ɗaya ta Musa, ɗaya kuma ta Iliya.” Bai ma san abin da yake faɗa ba.