Malachi 1:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا يَاثٜىٰ «طَا يَنَ غِرْمَمَ بَابَنْسَ، بَاوَ كُمَ يَنَ غِرْمَمَ مَيْغِدَنْسَ؞ تُواْ، عِدَنْ نِے بَابَنٜىٰ، إِنَا غِرْمَنَ؟ عِدَنْ كُمَ نِے مَيْغِدَا نٜىٰ، إِنَا دَرَجَتَ؟ يَا كُو ڢِرِسْتُواْثِے مَاسُ رٜىٰنَ سُونَنَ، كُكَثٜىٰ، ‹تَيَيَا مُكَ رٜىٰنَ سُونَنْكَ؟›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji Mai Runduna ya ce wa firistoci, “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bara kuwa yakan girmama maigidansa. Ni Ubanku ne, me ya sa ba ku girmama ni ba? Ni kuma Maigidanku ne, me ya sa ba ku ganin darajata? Kun raina ni, duk da haka kuna tambaya cewa, ‘Ƙaƙa muka raina ka?’