Malachi 2:15 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman ’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَشٜىٰ، بَ اللَّهْ نٜىٰ يَمَيْشٜىٰكُ جِكِے طَيَ دَ رُوحُ طَيَبَ؟ مٜىٰ اللَّهْ يَكٜىٰ نُڢِ دَ وَنَّنْ؟ يَنَسُواْ یَیَنْمُ سُذَمَ مَاسُ حَلِنْسَ؞ دُواْمِنْ حَكَ ڢَا، سَيْ كُلُورَ دَ كَنْكُ، كَدَ وَنِ عَثِكِنْكُ يَثِ أَمَانَرْ مَاتَرْسَ تَڧُرُثِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ashe, ba kai da ita Allah ya maishe ku jiki ɗaya da ruhu ɗaya ba? Me Allah yake nufi da wannan? Yana so 'ya'yanmu su zama 'yan halal masu tsoron Allah. Domin haka ku kula fa, kada kowa ya ci amanar matarsa ta ƙuruciya.