Mark 10:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ عِيسَىٰ ذَيْ تَاشِ يَبَرْ وُرِنْ كٜىٰنَنْ، سَيْغَا وَنِ مُتُمْ يَا ذُواْ دَ غُدُ، يَدُرْڧُسَ أَغَبَنْسَ، يَتَمْبَيٜىٰشِ يَثٜىٰ «مَلَمْ مَيْ كِرْكِ، مٜىٰ ذَنْيِ إِنْ سَامِ رَيْ نَهَرْ أَبَدَا؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya fara tafiya ke nan, sai ga wani ya sheƙo a guje, ya durƙusa a gabansa, ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?”