Mark 12:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ya shuka gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa rami domin matsin inabin, ya kuma gina ɗakin gadi. Sai ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, sa’an nan ya yi tafiya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِيسَىٰ يَڢَارَ يِمُسُ مَغَنَ دَ مِصَلَيْ؞ يَثٜىٰ «وَنِ مُتُمْ يَيِ غُواْنَرْ إِنَبِے، يَكٜىٰوَيٜىٰتَ دَ كَتَنْ‌غَ، يَحَڧَ وُرِنْ مَڟٜىٰوَرْ یَیَنْ إِنَبِنْ، يَكُمَ غِنَا طَاكِنْ مَيْغَادِ؞ يَبَا وَطَنْسُ مَنُواْمَ هَيَرْ غُواْنَرْ، سَعَنً يَتَڢِے وَتَ ڧَسَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Yesu ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ne ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabin, ya kuma gina wata 'yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma sufurin garkar, sa'an nan ya tafi wata ƙasa.