Mark 14:3 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عِيسَىٰ يَنَ بٜىٰتَنِ أَغِدَنْ وَنِ مُتُمْ وَنْدَ عَكٜىٰثٜىٰدَشِ سِيمَنْ مَيْ ثُوتَرْ ڢَتَرْ جِكِے؞ يَنَ ثِنْ عَبِنْثِ كٜىٰنَنْ، سَيْغَا وَتَ مَثٜىٰ تَذُواْ دَ وَتَ یَرْ ݣُولَبَرْ دَ عَكَيِ دَ دُوڟٜىٰنْ عُواْنِسْ ثِكٜىٰ دَ مَنْ ڧَنْشِ مَيْ ڟَادَ سُواْسَيْ وَنْدَ عَكَيِ دَ نَرْدِ ظَلَّ؞ سَيْ تَڢَشٜىٰ ݣُولَبَرْ تَظُبَ مَنْ عَكَنْ عِيسَىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana cin abinci ke nan, sai ga wata mace ta zo da wani ɗan tulu na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tsadar gaske. Sai ta fasa ulun, ta tsiyaye masa man a kā.