Mark 4:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِرِنْدَ يَڢَاطِ أَ حَنْيَ، شِينٜىٰ ݣُوتَنْثِنْ مُتَنٜىٰنْ دَ سُكَجِ كَلْمَرْ اللَّهْ ؞ عَمَّا دَظَرَرْ سُكَجِ، نَنْ دَنَنْ سَيْ شَيْطَنْ يَذُواْ يَطَوْكِ كَلْمَرْ دَ عَكَشُوكَ أَ ذُوثِيَارْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Waɗanda suka fāda a hanya kuwa, su ne kwatancin waɗanda aka shuka Maganar a zuciya tasu. Da zarar sun ji, nan da nan sai Shaiɗan ya zo ya ɗauke Maganar da aka shuka a zuciya tasu.