Mark 8:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَسَا تَارُوانْ مُتَنٜىٰ سُذَوْنَ عَڧَسَا؞ دَيَطَوْكِ غُرَاسَرْنَنْ بَݣَويْ، يَيِ غُواْدِيَ غَ اللَّهْ ، يَرَرَّبَ، يَيِ تَبَا أَلْمَجِرَنْسَ دُواْمِنْ سُبَا مُتَنٜىٰنْ، سُكَ كُوَ رَرَّبَ مُسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasan nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu.