Matthew 11:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ طَنْ مُتُمْ يَذُواْ يَنَثِ يَنَشَا، سُكَثٜىٰ، ‹غَا مَيْيَوَنْ ثِدَشَا، أَبُواْكِنْ مَاسُ كَرْٻَرْ هَرَاجِ دَ مَاسُ ذُنُوبِ!› دُكْدَهَكَ، أَنَ غَانٜىٰ حِكِمَرْ اللَّهْ أَعَيُّكَنْتَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’ Duk da haka hikimar Allah, ta aikinta ne ake tabbatar da gaskiyarta.”