Matthew 15:32 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَنَانً سَيْ عِيسَىٰ يَكِرَا أَلْمَجِرَنْسَ يَثٜىٰ «إِنَ جِنْ تَوْسَيِنْ جَمَعَرْ نَنْ، غَمَا يَوْ ݣُونَ عُكُ كٜىٰنَنْ سُنَ تَرٜىٰدَنِ، كُمَ بَاسُدَ عَبِنْثِ؞ بَانَسُواْ إِنْسَلَّمٜىٰسُ دَ يُنْوَ، دُواْمِنْ ذَاسُ عِيَ سُومَ أَ حَنْيَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yesu ya kira almajiransa, ya ce, “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna ba su da wani abinci. Ba na kuwa so in sallame su da yunwa haka, kada su kasa a hanya.”