Matthew 16:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
تُنْدَغَ وَنَّنْ لُواْكَثِ عِيسَىٰ يَڢَارَ نُونَ وَ أَلْمَجِرَنْسَ ثٜىٰوَ دُواْلٜىٰنٜىٰ يَجٜىٰ عُرُوشَلِيمَ، يَشَا وُيَ إِرِ إِرِ أَهَنُّنْ دَتَّاوَا دَ مَنْيَنْ ڢِرِسْتُواْثِے دَ مَلَمً كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى، عَكُمَ كَشٜىٰشِ، أَ رَانَ تَ عُكُ كُمَ عَتَاشٜىٰشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Tun daga lokacin nan Yesu ya fara bayyana wa almajiransa, lalle ne ya tafi Urushalima, ya sha wuya iri iri a hannun shugabanni da manyan firistoci da malaman Attaura, har a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.