Matthew 17:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin ’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَثٜىٰ «يَنَ بِيَ مَنَ؞» دَ بِتْرُسْ يَدَاوُاْ غِدَا، سَيْ عِيسَىٰ يَڢَارَ يِمَسَ مَغَنَ يَثٜىٰ «مٜىٰكَغَنِ غَمٜىٰدَ وَنَّنْ تَمْبَيَ؟ دَغَ وُرِنْ وَ سَرَاكُنَ سُكٜىٰ كَرْٻَرْ كُطِنْ هَرَاجِ دَغَ وُرِنْ یَیَنْسُ، كُواْ دَغَ وُرِنْ وَطَنْسُ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce, “I, yakan bayar.” Da ya dawo gida kuma, sai Yesu ya fara yi masa magana ya ce, “Me ka gani, Bitrus? Wurin wa sarakunan duniya suke karɓar kuɗin fito ko haraji, a wurin 'ya'yansu, ko kuwa daga wurin waɗansu?”