Matthew 17:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنَ مَغَنَ كٜىٰنَنْ سَيْغَا وَنِ غِرْغِجٜىٰ مَيْ حَصْكٜىٰ يَرُڢٜىٰسُ، عَكَ كُمَ جِ وَتَ مُرْيَ دَغَ ثِكِنْ غِرْغِجٜىٰنْ تَثٜىٰ «وَنَّنْ شِينٜىٰ طَانَ، وَنْدَ نَكٜىٰ ڧَوْنَ، إِنَ جِنْ دَاطِنْسَ ڨُورَيْ؞ كُسَوْرَرٜىٰشِ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yana magana ke nan sai ga wani gajimare mai haske ya zo ya rufe su. Aka kuma ji wata murya daga cikin gajimaren, ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai. Ku saurare shi.”