Matthew 2:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ هِرُدُسْ يَغَانٜىٰ ثٜىٰوَ مَاسُ عِلِمِنَّنْ سُنْيِ مَسَ وَيُواْ نٜىٰ، سَيْ يَيِ ڢُشِے سُواْسَيْ؞ يَعَيْكَ عَكَكَّشٜىٰ دُكَنْ یَنْ يَارَا مَظَا وَطَنْدَ سُكٜىٰ ثِكِنْ بَيْتَلَحْمِ دَ كٜىٰوَيٜىٰنْتَ دَغَ مَاسُ شٜىٰكَرَا بِيُ ذُوَا ڧَسَا، ڠُورْڠُودُوانْ لُواْكَثِنْ دَ مَاسُ عِلِمِنَّنْ سُكَ ڢَطَا مَسَ غَمٜىٰدَ يَرُوانْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Hirudus ya ga masanan nan sun mai da shi wawa, sai ya hasala ƙwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan nan.