Matthew 27:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ بِلَتُسْ يَذَوْنَ أَوُرِنْ شَرِيعَ، سَيْ مَاتَرْسَ تَ عَيْكُواْ عَثٜىٰمَسَ «كَڢِتَ شَعَنِنْ مَرَرْ لَيْڢِنَّنْ، دُواْمِنْ يَوْ نَشَا وَهَلَ سُواْسَيْ أَمَڢَرْكِ عَكَنْسَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Banda haka kuma, a lokacin da yake zaune a kan gadon shari'a, sai mata tasa ta aiko masa da cewa, “Ka fita daga sha'anin mara laifin nan, don yau na sha wahala ƙwarai a mafarkinsa.”