Matthew 27:24 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ بِلَتُسْ يَغَ بَا أَبِنْدَ ذَيْ عِيَيِ، كُمَ مُتَنٜىٰنْ سُنَ شِرِنْ تَادَ حَنْكَلِ، سَيْ يَطٜىٰبِے ضُوَ يَوَنْكٜىٰ حَنُّوَنْسَ أَغَبَنْ مُتَنٜىٰ، يَثٜىٰ «نِے دَيْ، بَا ضُوَنَ دَ أَلْحَكِنْ جِنِنْ مَرَرْ لَيْڢِنَّنْ؞ وَنَّنْ ضُوَنْكُ نٜىٰ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Bilatus ya ga bai rinjaye su ba, sai dai hargitsi yana shirin tashi, sai ya ɗibi ruwa ya wanke hannunsa a gaban jama'a, ya ce, “Ni kam, na kuɓuta daga alhakin jinin mai adalcin nan. Wannan ruwanku ne.”