Matthew 4:18 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عِيسَىٰ يَنَ تَڢِيَ أَغٜىٰڢٜىٰنْ تٜىٰكُنْ غَلِيلِ كٜىٰنَنْ، سَيْ يَغَ وَطَنْسُ یَنْعُوَ غُدَا بِيُ، سِيمَنْ دَ عَكٜىٰثٜىٰ دَشِ بِتْرُسْ دَ طَنْعُوَنْسَ أَنْدَرَوُسْ، سُنَ جٜىٰڢَ رَاغَرْ كَامُنْ كِيڢِ عَتٜىٰكُ، دُواْمِنْ سُو مَاسُ كَامُنْ كِيڢِ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yana tafiya a bakin Tekun Galili ke nan, sai ya ga waɗansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, don su masunta ne.