Micah 4:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يِبِرْغِمَ ثِكِنْ ذَاڢِ دَ نِيشِ، يَا كٜىٰ ذُوثِيَاتَ سِهِيُواْنَ، كَمَرْ مَثٜىٰ مَيْجِ دَ ذَاڢِنْ حَيْڢُوَ؞ غَمَا يَنْذُ ذَاكِ ڢِتَ دَغَ بِرْنِ، كِذَوْنَ عَتٜىٰنْتِ عَبَايَنْ غَرِ، ذَاكِ تَڢِے بَابِيلَ؞ دَغَ ثَنْ نٜىٰ يَهْوٜىٰهْ ذَيْڢَنْشٜىٰكِ دَغَ حَنُّنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْكِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ki yi makyarkyata, ki yi nishi, ke Sihiyona, Kamar mace mai naƙuda, Gama yanzu za ki fita daga cikin birni, Ki zauna a karkara, Za ki tafi Babila, daga can za a cece ki. Daga can Ubangiji zai cece ki daga hannun maƙiyanki.