Micah 4:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ مَيْدَ غُرَغُ ضَغُواْوَرْ جَمَعَتَ، وَطَنْدَ عَكَ كُواْرَ كُمَ أَلْعُمَّ مَيْ ڧَرْڢِے؞ نِے يَهْوٜىٰهْ ذَنْيِ مُلْكِنْسُ عَتُدُنْ سِهِيُواْنَ، دَغَ يَنْذُ ذُوَا حَرْ أَبَدَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan sa guragu su wanzu, Korarru kuwa su zama al'umma mai ƙarfi, Ni, Ubangiji, zan yi mulkinsu a Sihiyona har abada.