Micah 5:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Za su yi mulkin ƙasar Assuriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma da zaran takobi. Zai cece mu daga hannun Assuriyawa sa’ad da suka kawo wa ƙasarmu hari suka kuma tattake zuwa cikin iyakokinmu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ تَكُواْبِے، شُوغَبَنِّنَّنْ ذَاسُيِ مُلْكٍ ڧَسَرْ أَسُّرِيَ، ڧَسَرْ نِمْرُوادْ كُمَ دَ بَاكِنْ تَكُواْبِے؞ تَهَكَ مَيْ مُلْكٍ ذَيْ كُٻُتَرْ دَمُو دَغَ حَنُّنْ أَسُّرِيَاوَا، سَعَدَّ سُكَ كَٰوُاْ وَ ڧَسَرْمُ يَاڧِ، كُواْ سُشِغَ بَاكِنْ إِيَاكَرْ ڧَسَرْمُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za su mallaki ƙasar Assuriya da takobi, Su shiga ƙofofin ƙasar Nimrod da zararren takobi, Zai cece mu daga hannun Ba'assuriye, Sa'ad da ya kawo wa ƙasarmu yaƙi, Sa'ad da kuma ya tattake ƙasarmu.