Nehemiah 1:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا عُبَنْغِجِ ، بَرِ كَكَسَ كُنّٜىٰ كَجِ أَدُّعَرْ بَاوَنْكَ دَ كُمَ أَدُّعَرْ سَوْرَنْ بَايِنْكَ، وَطَنْدَ سُكٜىٰ جِنْ دَاطِنْ غِرْمَمَ سُونَنْكَ؞ بَرِ كَبَا بَاوَنْكَ نَصَرَا يَوْ، كَسَا سَرْكِے يَيِ مَسَ جِنْڧَيْ؞» أَ لُواْكَثِنْ، مَڟَيِنَ نَمَيْمِيڧَا وَسَرْكِے أَبِنْ شَا نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu'ar bawanka, da addu'o'in bayinka, waɗanda suke jin daɗin girmama sunanka. Ka ba bawanka nasara yau ka sa ya sami tagomashi a gaban mutumin nan.”