Nehemiah 1:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَرِ كَكَسَ كُنّٜىٰ، كَدُوبٜىٰنِ، كَجِ أَدُّعَرْ بَاوَنْكَ، وَدَّ نَكٜىٰيِ عَيَنْظُ دَرٜىٰ دَ رَانَ أَغَبَنْكَ؞ إِنَ يِنْ أَدُّعَ أَمَدَدِنْ بَايِنْكَ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا، إِنَ ڢُرْتَ مَكَ ذُنُبَنْدَ مُو جَمَعَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ مُكَيِ؞ لَلَّيْ نِے دَ كَاكَنِّنَ مُنْيِ مَكَ ذُنُوبِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ina roƙonka ka kasa kunne, ka kuma buɗe idanunka, ka ji addu'ar bawanka, wadda nake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra'ila. Ina hurta zunubanmu, mu mutanen Isra'ila, da muka yi maka. Ni da gidan ubana mun yi zunubi.