Nehemiah 11:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
شُوغَبَنِّنْ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ كُوَ سُكَ ذَوْنَ أَ عُرُوشَلِيمَ؞ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰنْ كُمَ سُكَجٜىٰڢَ ڧُرِعَ دُواْمِنْ عَكَٰوُاْ عِيَلِ طَيَ دَغَ ثِكِنْ كُواْوَنٜىٰ عِيَلِ غُواْمَ سُذَوْنَ عَثِكِنْ عُرُوشَلِيمَ بِرْنِ مَيْ ڟَرْكِے؞ عَمَّا عَكَ بَرْ سَوْرَنْ عِيَلَيْ تَرَ دَغَ ثِكِنْ غُواْمَ سُذَوْنَ أَغَرُرُوَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Shugabannin jama'a kuwa suka zauna a Urushalima. Sauran jama'a kuma suka jefa kuri'a don a sami mutum guda daga cikin goma wanda zai zauna a Urushalima, wato tsattsarkan birni, sauran tara kuwa su yi zamansu a sauran garuruwa.