Nehemiah 13:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da ’ya’yanku mata aure ga ’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri ’ya’yansu mata wa ’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نَيِ وَمُتَنٜىٰنْ ڢَطَ سُواْسَيْ، نَلَعَنْتَسُ، نَدُوكٜىٰ وَطَنْسُنْسُ، نَثِثِّرٜىٰ غَاشِنْ كَنْسُ؞ سَيْنَسَا سُرَنْڟٜىٰ دَ سُونَنْ اللَّهْ ثٜىٰوَ بَذَاسُ ڧَارَ بَادَ یَیَنْسُ مَتَ غَ یَیَ مَظَا نَوَطَنْدَ بَا يَهُودَاوَا بَ سُعَوْرَ، كُواْ یَیَنْسُ مَظَا كُواْ سُو كَنْسُ سُعَوْرِ یَیَنْ مَاتَا وَطَنْدَ بَا يَهُودَاوَا بَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai na yi musu faɗa na la'ance su, na bugi waɗansu daga cikinsu, na ciccire gashin kansu, na sa su rantse da Allah, cewa ba za su aurar da 'ya'yansu mata ga 'ya'yan maza na bare ba, ko kuma su auro wa 'ya'yansu maza 'yan matan bare, ko su auro wa kansu.