Nehemiah 4:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don ’yan’uwanku, da ’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ نَدُوبَ يَدَّ أَبُبُوَنْ سُكٜىٰ، سَيْ نَتَاشِ نَتَارَ مَنْيَنْ مُتَنٜىٰ دَ دَتَّاوَا دَ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰ؞ نَثٜىٰ «كَدَ كُجِڟُواْرُوانْ أَبُواْكَنْ غَابَنْمُ؞ كُتُنَ عُبَنْ‌غِجِ مَيْغِرْمَ نٜىٰ، مَيْ بَنْ ڟُواْرُواْ كُمَ؞ كُيِ يَاڧِ دُواْمِنْ كُڟَرٜىٰ یَنْعُوَنْكُ دَ یَیَنْكُ مَظَا دَ مَاتَادَ مَاتَنْكُ دَ كُمَ غِدَاجٜىٰنْكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da na ga mutane sun damu, sai na tashi na yi magana da shugabanni, da sauran jama'a, na ce, “Kada ku ji tsoro, ku tuna da Ubangiji mai iko, mai banrazana, ku yi yaƙi domin 'yan'uwanku, da 'ya'yanku mata da maza, da matanku, da gidajenku.”