Nehemiah 5:15 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڠُومْنُواْنِنْ دَ سُكَ رِغَانِ سُنْ بَا مُتَنٜىٰ وَهَلَ سُواْسَيْ تَوُرِنْ كَرْٻَرْ عَبِنْثِ دَ ضُوً إِنَبِے دَغَ غَرٜىٰسُ، بَنْدَ كُطِنْ أَظُرْڢَا أَرْبَعِنْ؞ حَرْ مَا سَمَارِ مَاسُ يِمُسُ عَيْكِ سُكَ نُونَ وَمُتَنٜىٰنْ إِيكُواْ؞ عَمَّا نِے بَنْ يِهَكَبَ سَبُواْدَ إِنَ ڟُواْرُوانْ اللَّهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Waɗanda suka riga ni mulki sun nawaita wa mutane. Sun yi ta karɓar abinci da ruwan inabi daga gare su, banda shekel arba'in kowace rana domin abinci da ruwan inabi. Har ma barorin masu mulki sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.