Nehemiah 7:3 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نَڢَطَا مُسُ ثٜىٰوَ كَدَ عَبُوطٜىٰ ڧُواْڢُواْڢِنْ عُرُوشَلِيمَ دَ سَڢٜىٰ سَيْ بَايَنْ رَانَ تَهَوْ؞ كُمَ كَاڢِنْ مَاسُ غَادِنْ ڧُواْڢُواْڢِ سُتَاشِ دَغَ عَيْكِ وَجٜىٰنْ ڢَاطُوَرْ رَانَ، سَيْ سُرُڢٜىٰ ڧُواْڢُواْڢِ سُكُلّٜىٰ دَ سَكَتَ؞ نَڧَارَ دَ ثٜىٰوَ سُذَاٻِ مَاسُ غَادِ دَغَ ثِكِنْ مَذَوْنَنْ عُرُوشَلِيمَ دُواْمِنْ سُيِ غَادِنْ أَوُرَارٜىٰنْ غَادِ، وَطَنْسُ كُمَ سُيِ غَادِنْ سَاشٜىٰنْ كَتَنْغَرْ نَغَبَنْ غِدَاجٜىٰنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan na ce musu, kada su buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe, sai rana ta cira sosai, su kuma kulle ƙofofin da ƙarfe kafin matsara su tashi wajen faɗuwar rana. Su samo matsara daga mazaunan Urushalima, su sa su tsaye a muhimman wurare, waɗansunsu kuma suna zaga gidaje.