Nehemiah 8:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ نٜىٰهٜىٰمِيَ يَثٜىٰ مُسُ «كُكُواْمَ غِدَا، كُثِ عَبِنْثِ مَيْݣَوْ، كُشَا كَايَنْ ذَاڧِ؞ كُعَيْكَ وَ وَطَنْدَ بَاسُ دَكُواْمٜىٰ؞ غَمَا وَنَّنْ رَانَ مَيْ ڟَرْكِے ثٜىٰ غَ عُبَنْ‌غِجِنْمُ ؞ سَبُواْدَ حَكَ كَدَ كُيِ بَڧِنْ ثِكِ، غَمَا ڢَضٍ ثِكِنْ دَ كُكٜىٰ دَشِ ثِكِنْ يَهْوٜىٰهْ شِينٜىٰ تُوشٜىٰنْ ڧَرْڢِنْكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan ya ce musu, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha ruwan inabi mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi, gama wannan rana tsattsarka ce ta Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin da Ubangiji ya ba ku shi ne ƙarfinku.”