Nehemiah 8:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مُتَنٜىٰ سُكَ تَڢِے سُكَ كَٰوُاْ رَسَّنْ عِتَتُوَ سُكَ كُمَ شِرْيَ وَكَنْسُ بُكُّواْكِ عَكَنْ رُڢِنْ غِدَاجٜىٰنْسُ دَ كُمَ ثِكِنْ ڢِيلِنْ غِدَاجٜىٰنْسُ دَ ثِكِنْ ڢِيلِ عَثِكِنْ غِدَنْ اللَّهْ دَ ثِكِنْ ڢِيلِنْ دَيَكٜىٰ غَبَنْ ڧُواْڢَرْ ضُوَ دَ ثِكِنْ ڢِيلِنْ دَيَكٜىٰ غَبَنْ ڧُواْڢَرْ إِڢْرَيِمْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai suka tafi suka kawo rassan, suka yi wa kansu bukkoki a kan rufin sorayensu, da a dandalinsu, da cikin harabar Haikalin Allah, da a dandalin Ƙofar Ruwa, da a dandalin Ƙofar Ifraimu.