Nehemiah 8:18 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُواْوَثٜىٰ رَانَ كُوَ عُزَيْرُ يَكَنْ كَرَنْتَ دَغَ ثِكِنْ نَطَطّٜىٰنْ لِتَّڢِنْ كُواْيَرْوَرْ اللَّهْ ، تُنْدَغَ رَانَ تَڢَرْكُواْ تَبِكِ حَرْ ذُوَا رَانَ تَڧَرْشٜىٰ؞ سُكَيِ بِكِنَّنْ حَرْ ݣُونَ بَݣَويْ، أَ رَانَ تَتَݣُوسْ عَكَيِ مُهِمِّنْ تَارُواْ بِسَغَ ڧَٰعِدَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kowace rana, tun daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra yakan karanta musu daga cikin littafin dokokin Allah. Suka kiyaye idin har kwana bakwai. A rana ta takwas kuma suka muhimmin taro bisa ga ka'ida.