Nehemiah 8:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عُزَيْرُ يَيَبِے يَهْوٜىٰهْ ، اللَّهْ مَيْغِرْمَ؞ دُكَنْ جَمَعَرْ كُوَ سُكَ أَمْسَ «أَمِينْ! أَمِينْ!» سُنَ طَغَ حَنُّوَنْسُ سَمَ؞ سُكَ رُسُنَ دَ ڢُسْكُواْكِنْسُ حَرْ ڧَسَا، سُكَيِ وَ يَهْوٜىٰهْ سُجَّدَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Ezra ya yabi Ubangiji Allah Maɗaukaki. Jama'a duka suka amsa, “Amin, amin!” suna ɗaga hannuwansu. Suka sunkuyar da kansu har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada.