Nehemiah 9:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَا عَيْكَتَ عَلَمُ دَ أَيُّكَنْ بَنْ مَامَاكِ عَكَنْ سَرْكِے ڢِرْعَوْنَ دَ دَتَّاوَنْسَ دَ مُتَنٜىٰنْ ڧَسَرْسَ، غَمَا كَاسَنْ يَدَّ سُكَ دَنّٜىٰ كَاكَنِّنْمُ؞ تَهَكَ كَيِ سُونَ، سُونَنْ دَ كَكٜىٰ دَشِ حَرْ يَوْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ka kuma aikata alamu da al'ajabai a kan Fir'auna, Da fadawansa duka, da mutanen ƙasarsa, Gama ka san yadda suka yi wa jama'arka danniya. Ta haka ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau.