Nehemiah 9:24 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
یَیَنْسُ سُكَ شِغَ سُكَ مَلَّكِ ڧَسَرْ كَنْعَنَ، كَا شَا غَبَنْسُ كَاثِ ڧَبِيلُنْ ڧَسَرْدَ يَاڧِ؞ كَا بَادَ مَذَوْنَنْ كَنْعَنَ أَ حَنُّنْسُ، دَ ڧَبِيلُ دَ سَرَاكُنَنْ دُكَ، سُيِ مُسُ يَدَّ سُنْ غَ دَامَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan'ana. Ka rinjayi mutanen da suke zama a can. Ka ba jama'arka iko su yi yadda suke so Da mutane, da sarakunan ƙasar Kan'ana.