Nehemiah 9:27 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَبُواْدَ حَكَ كَبَادَسُو أَ حَنُّنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ وَطَنْدَ سُكَ دَنّٜىٰسُ؞ أَ ذَمَنْ دَنِّيَرْسُ، مُتَنٜىٰنْكَ سُكَيِ كُوكَا غَرٜىٰكَ، كَيْ كَكُوَ جِيسُ دَغَ سَمَ؞ بِسَغَ يَوَنْ جِنْڧَنْكَ كَعَيْكَ مُسُ مَاسُ ثٜىٰتُواْ وَطَنْدَ سُكَثٜىٰثٜىٰسُ دَغَ حَنُّنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Saboda haka ka bar abokan gābansu su ci su, mallake su. A wahalarsu sun yi kira gare ka domin taimako, Ka kuwa amsa musu daga Sama. Ta wurin jinƙanka mai yawa ka aiko musu da shugabanni, Waɗanda suka kuɓutar da su daga maƙiyansu.