Nehemiah 9:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ وَطَنَّنْ لَوِيَاوَا وَتُواْ، يٜىٰشُوَ دَ كَدْمِيٜىٰلْ دَ بَنِ دَ هَشَبْنٜىٰيَ دَ شٜىٰرٜىٰبِيَ دَ هُواْدِيَ دَ شٜىٰبَنِيَ دَ ڢٜىٰتَهِيَ سُكَيِ كِرَنْ سُجَّدَ سُكَثٜىٰ، «تَاشِ ڟَيٜىٰ كُيَبِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ، اللَّهْ نْكُ مَرَرْ ڢَرْكُواْ مَرَرْ ڧَرْشٜىٰ!» «أَلْبَرْكَ تَا تَبَّتَا غَ سُونَنْكَ مَيْ دَرَجَ، سُونَنْدَ يَڢِ دُكَنْ أَلْبَرْكَ دَ يَبُواْ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce, “Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku, Ku yabe shi har abada abadin. Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii, Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”