Numbers 10:29 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مُوسَٰى يَيِ مَغَنَ دَ هُواْبَبْ طَنْ يِتْرُواْ مُتُمِنْ مَدْيَنَ، بَابَنْ مَاتَرْ مُوسَٰى، يَثٜىٰ «يَنْذُ ڢَا، مُنَ شِرِنْ تَاشِ دَغَ نَنْ مُكَامَ حَنْيَ ذُوَا وُرِنْ دَ يَهْوٜىٰهْ يَيِ مَنَ أَلْڧَوَرِ ثٜىٰوَ ذَيْبَامُ؞ كَذُواْ مُتَڢِے تَرٜىٰ، ذَامُيِ مَكَ أَلْحٜىٰرِ غَمَا يَهْوٜىٰهْ يَيِ أَلْڧَوَرِ ثٜىٰوَ ذَيْ يِوَ إِسْرَٰٓءِيلَ أَلْحٜىٰرِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra'ila alheri.”