Numbers 11:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?” ’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا ذَاسُدِنْغَ ثِنْ نَامَ حَرْ وَتَا طَيَ، حَرْ سَيْ يَڢِتَ مُسُ أَهَنْثِ، حَرْ مَا سَيْ سُنْڧِے غَنِنْسَ؞ وَنَّنْ ذَيْ ڢَرُ حَكَ، غَمَا سُنْڧِے يَهْوٜىٰهْ وَنْدَ يَكٜىٰ عَثِكِنْسُ، سُنَ كُمَيِتَيِنْ كُوكَا أَغَبَنْسَ ثٜىٰوَ ‹مٜىٰيَسَا مُكَ بَرْ مَصَرْ؟› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma har wata guda cur. Za su ci har ya gundure su, ya zama musu abin ƙyama saboda sun ƙi Ubangiji wanda yake tare da su, suka yi gunaguni a gabansa, suna cewa, ‘Me ya sa ma, muka fito Masar?’ ”