Numbers 11:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَݣَويْ وَطَنْسُ دَتَّاوَا غُدَا بِيُ وَطَنْدَ بَسُ تَڢِے غَبَنْ تٜىٰنْتِنْ تَرٜىٰدَ سَوْرَنْ دَتَّاوَنْ بَ، سُونَيٜىٰنْسُ كُوَ عٜىٰلْدَدْ دَ مٜىٰدَدْ نٜىٰ؞ سُنَ ثِكِنْ وَطَنْدَ عَكَ لِسَّڢْتَا، عَمَّا سُنَ ثِكِنْ ذَنْغُواْ تُكُنَ أَ لُواْكَثِنْ دَ رُوحُ يَسَوْكَ، سَيْ سُو مَا سُكَيِ أَنَّبْثِ دَ إِيهُ دَ ضَوَ عَثِكِنْ ذَنْغُوانْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Akwai mutum biyu da suka ragu a zangon, sunan ɗayan Eldad, ɗayan kuwa Medad. Ruhun kuma ya zauna a kansu gama suna cikin dattawan nan da aka lasafta, amma ba su fita zuwa alfarwa ba, sai suka yi annabci a zangon.