Numbers 16:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan ’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا مُوسَٰى دَ هَٰرُونَ سُكَ ڢَاطِ دَ ڢُسْكَرْسُ حَرْ ڧَسَا سُكَثٜىٰ «يَا اللَّهْ ، كَيْنٜىٰ اللَّهْ ، تُوشٜىٰنْ نُمْڢَشِنْ رَيْ نَدُكَنْ حَلِتَّ؞ إِنْ مُتُمْ طَيَ يَيِ ذُنُوبِ، ذَاكَيِ ڢُشِے دَ دُكَنْ جَمَعَ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki, suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin 'yan adam duka, za ka yi fushi da dukan taron jama'a saboda zunubin mutum ɗaya?”