Numbers 21:24 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا إِسْرَٰٓءِيلَاوَا سُكَ يَاڧٜىٰشِ سُكَ كَكَّشٜىٰ دَيَوَ دَغَ ثِكِنْسُ دَ تَكُواْبِے، سُكَ كُمَ مَلَّكِ ڧَسَرْسُ، تُنْدَغَ كُواْغِنْ أَرْنُوانْ ذُوَا أَرٜىٰوَ حَرْ كُواْغِنْ يَبُّواكْ، عَمَّا سُنْ ڟَيَ عَ إِيَاكَرْ يَنْكِنْ أَمُّواْنَاوَا، غَمَا أَنْڟَرٜىٰ إِيَاكَرْ يَنْكِنْ أَمُّواْنَاوَا دَ ڧَرْڢِے سُواْسَيْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Isra'ilawa kuwa suka karkashe su da takobi, suka mallaki ƙasarsa tun daga Kogin Arnon zuwa Kogin Yabbok, har zuwa kan iyakar Ammonawa, gama Yahaza ita ce kan iyakar Ammonawa.