Numbers 21:34 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ كُوَ يَثٜىٰ وَ مُوسَٰى «كَدَ كَجِڟُواْرُوانْسَ، غَمَا نَارِغَا نَا بَادَشِ أَ حَنُّنْكَ، دُكْ دَ سُواْجُواْجِنْسَ دَ ڧَسَرْسَ؞ كَيِمَسَ يَدَّ كَيِ وَ سَرْكِے سِهُوانْ نَ أَمُواْرِيَاوَا، وَنْدَ دَا يَيِ مُلْكِ أَ هٜىٰشْبُوانْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na bashe shi a hannunka duk da jama'arsa, da ƙasarsa. Za ka yi masa yadda ka yi wa Sihon, Sarkin Amoriyawa wanda ya zauna a Heshbon.”